Kotun koli ta dage zaman yanke hukuncin zaben Gwamnonin Sokoto,Kano,Imo,Plateau Bauchi da Benue

A labarin duminsa ya bayyana cewa cinkoson jama’a sosai da kuma surutunsu ya sanya kotun Kolin Nijeriya ta dage zaman da ta fara yau na yanke hukuncin shari’ar zaben wasu gwamnonin Nijeriya da ta fara yi a yau.

Alkalin-Alkalan Nijeriya Mai Shari’a Ibrahim Tanko dake jagorantar masu shari’a 7 ne ya bayyana dage zaman a zauren kotun Kolin.

Ya kuma bayyana wa masu kara da wadanda ake kara kada kowannensu ya wuce lauyoyi biyar, da kuma wakilan jamiyya kadai a zama na gaba

Za a iya tuna cewa da a yau ne kotun ke yanke hukuncin shari’ar zaben gwamnan jihar Kano, da Sokoto, da Plateau da Imo da Bauchi da da Benue .

Za a cigaba da zaman zuwa gobe talata

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment