An zuma yan sanda a Sokoto saboda shari’ar gwamna da kotun Koli za ta yanke hukunci gobe

Rundunar yan sandan Nijeriya reshen jihar Sokoto ta bayyana cewa a yanzun haka ta barbaza jami’aat a kalla guda 1000 a cikin gari da kewayen jihar, bisa tabbatar da kyakkyawan tsaro bayan Kotun Koli ta yi hukuncin karshe kan wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka yi a 2019.


Dan takarar jam’iyyar APC Ahmed Aliyu ne ya shigar da zababben gwamnan jihar Tambuwal na jamiyyar PDP a kotun yana kalubalntar nasarar da ya samu.

A gobe Litinin ne dai ake sa ran babbar kotun Kolin Nijeriya za ta yi hukunci na karshe a kan halastatcan gwamnan na jihar Sokoton

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment