An cimma yarjejeniyar tsagiata bude wuta a Libiya

Gwamnatin hadin kan kasa a Libiya ta cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta da dakarun sojin Janar Khalifa Haftar da ke kan bakansu na kwace iko da babbab birnin kasar.

Bangarorin biyu da suka dau lokaci suna gwabza fada kan iko da Tripoli sun cimma matsaya na dakatar da fada bayan da wata yarjejeniya da kasashen Turkiyya da Rasha suka shiga tsakani.

Sai dai Janar Haftar ya ja kunnen bangaren gwamnatin da ke samun goyon abyan Majalisar Dinkin Duniya za su su fuskanci martani mai tsanani idan suka yi karambanin sake tada rikici.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment