Buhari ya dauki matakin gaggawa bayan Gov, Zulum ya kwana cikin yan gudun hijira

Shugaba Muhammadu Buhari ya bayar da kwangilar gina gidaje 10,000 a jihar Borno a cikin yunkurin da gwamnatin tarayya ke yi na farfado da jihar bayan barnar da ta’addancin Boko Haram ya yi.


Gwamnan jihar Borno, Babagana Umaru Zulum ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a 10 ga watan Janairu a shafinsa na Twitter.

Shugaban kasar ya yi wannan umurnin ne bayan Zulum ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira a ranar Alhamis, 9 ga watan Janairu inda ya kwana a can yana taimakawa wurin rabon kayan tallafi ga kimanin iyalai 1675.

Gwamnan ya kuma yi rabon barguna da daduma ga ‘yan yi wa kasa hidima a jihar don taimaka musu magance sanyi a wannan yanayin na hunturu.

Ya kuma tabbatarwa ‘yan gudun hijirar cewa yana nan kan bakansa na kokarin ganin an mayar da su garuruwansu idan an gama gine-gine.

Kazalika, Zulum ya yi wa ‘yan gudun hijiran alkawarin cewa gwamnatin tarayya na iya kokarin ta don ganin ta kawoi karshen ta’addanci a jihar da sauran sassan kasar.

Gwamnan jihar na Borno ya kuma yabawa rundunar sojojin Najeriya kan matakin da ta dauka na gudanar da bincike kan zargin karbar kudade a hannun matafiya da ake ce sojoji na yi.

Majiyarmu ga Legit. ng ta gano cewa Zulum ya yi wannan jawabin ne a daren Litinin 6 ga watan Janairu bayan mai kula da fanin yada labarai na soji, Aminu Iliyasu ya fitar da sanarwa.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment