Fadar Najeriya ta nesanta Buhari da hannu a kudirin kara wa’adin mulki

Fadar mulkin Najeriya ta fitar da sanarwar da ke nesanta shugaba Muhammadu Buhari da hannu wajen gabatar da kudirin da ke shirin mayar da tsarin kowanne wa’adi na mulkin kasar zuwa shekaru 6, kudirin da ya sha kaye a gaban majalisun kasar cikin makon jiya.

Cikin sanarwar fadar ta bayyana cewa guda cikin ‘yan Majalisar wakilai da ta kira sunanshi da Mr John Dyegh ne ya gabatarwa Majalisar kudirin, kuma ko da majalisar ta aminta da kudirin ba zai fara aiki ba sai bayan gushewar gwamnati mai ci shekarar 2023.

A cewar babban mataimaki na musamman ga shugaba Muhammadu Buhari kan al’amuran da suka shafi Majalisa Senator Babajide Omoworare, ya bayyana cewa shugaban Najeriyar ya sha nanata rashin bukatar shi ta kara koda kwana guda a mulki bayan karewar wa’adinsa, hasalima ya sha alwashin kin mara baya ga kowanne dan siyasa yayin zaben shekarar 2023.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

One thought on “Fadar Najeriya ta nesanta Buhari da hannu a kudirin kara wa’adin mulki

Leave a comment