Gwamnatin Jahar Zamfara za ta dauki Matasa 2000 karkashi hukumar ZAROTA.

Gwamnatin jahar Zamfara za ta samawa matasa dubu biyu aikin yi a karkashin Hukumar Rage Cinkoson Ababen Hawa akan Hayoyin Jahar, mai suna ZAMFARA STATE ROAD TRAFIC AGENCY (ZAROTA).


Sabon kwamandan hukumar na jahar Alhaji Aliyu Alhazzai Shinkafi ya sanar da hakan, a zantawarshi da manema labarai a garin Gusau dake cikin jahar Zamfara.

Alhaji Aliyu Alhazzai ya bayyana cewa matasa dubu biyu da Hukumar za ta dauka aiki, kari ne a kan daruruwan matasan da suka dauki dogon lokaci suna bautawa al’umar Jahar a karkashin wannan hukuma ta ZAROTA a cikin jahar.

Kwamandan hukumar ya yi bayanin cewa, za a soma biyan dukkanin matasan da hukumar ta dauka aiki, domin samun nasarar kawar da zaman kashe wando da ya yi wa wasu matasan jahar katutu a wannan lokacin.

Da ya juya a kan dangantakar hukumar ZAROTA da sauran hukumomin tsaro dake aiki a cikin Jahar, Alhaji Shinkafi ya ce,Hukumar ZAROTA tare da Hadin Gwiwar sauran Hukumomin Tsaro, za su dauki matakin kawar da cinkaso da ake fuskanta a wasu manyan garuruwa na jahar ta hanyar gudanar da kasuwanci akan hanyar mota.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment