Aikin Hajji a saukake /Jekadiyar Zamfara

Da Sunan Allah, Salati da Sallama su tabbata ga Manzo da Iyalansa da Sahabbai.

Daga: Sheak Abdulhakeem Ahmad Ya’akub Gusau.

Kasancer aikin Hajji, ba rana daya akeyinsa ba

Don haka zanyi bayanin dai dai da ranakun aikin:

RANAR 8, GA WATA

Ana fara aikin Hajji ne, ranar takwas ga watan Zulhajj, ana karanta (Yaumu Tarwiyati)

A wannan rana mai Hajjin Tamattu’i, zai daura Harma da Hajji da Hantsi

1. Zaiyi wanka, da duk abinda yayi lokacin Umra

Na gusar da gashi, cire kumba, daura Harami da sauran su

2. Zai yi niyya da Hajji, kamar yadda lokacin Umra, illah a wannan Niyar Hajji zai yi

Zai CE: Labbaika Hajjan, bayan kuma yayi Niya a zuciya

Ko Nawaitul Hajja Wa’ahramtu bihi lillahi Ta’alah

Idan yakara da: Rabbana Taqabbal miniy ba komi

3. Daga za’kawo motoci a daukeku zuwan filin Mina

Za’atafi ne, ana Talbiya(Labbaikallahumma Labbaik…)

4. An so zuwa filin Mina kafin rana ta karkata,(Zawwal)

Idan an sa6a dai ba komi, amma dai a yawaita Talbiya

5. Za’ayi Sallolin Azuhur da La’asar da Magrib da Isha’i

Sai dai Azuhur da La’asar da Isha’i kowace raka’a 2, amma a lokacin ta

6. Za’a kwana anan har gari ya waye, rana ta fito, sai a tasamma arafa

RANAR 9, GA WATA, WUNIN ARFA

A Wannan rana ne, ake tsayuwar Arfa

1. Za’a tafi ana Talbiya har a isa a cikin filin Arfa

Idan akaje Arfa, anso a sauka Namira, idan yayiwu, inbai samuba duk Inda ka tsaya yayi

Sai dai wurinda ake kira da (Badni Uranata) ba’atsuya nan

2. Idan rana ta karkata (Zawwal)
za’ayi Sallolin Azuhur da La’asar tare

Za’ayi su a jam’i, kowace raka’a 2, kiran Sallah 1, ikama 2

Anso a saurari Khuduba daga Limamin arfa, don jin hukunce hukuncen Hajj

Daga nan tsayuwar Arfa zata fara, har faduwar rana

3. Tsayuwar Arfa, na nufin kasancewar Alhaji a filin Arfa, ana addua da zikrori

Daga karkatawar rana zuwa faduwarta, a tsaye ko zaune koma kwance

Koda mutum baya lafiya, yazo filin yazauna koda baisan ankawo shi ba, tsayuwarsa tayi

Ko rana ta fadi, mutum bai zo Arfa ba, bata kubce masa sai alfijir ya hudo

Ana son yawaita addua fiyeda ko’ina, da tuba da kuka da kastastarda kai ga Allah

Yazo a Hadisi, yana cikin mafi girma Zunubi mutum yayi tsayuwar
Arfa yayi tunanin ba’a Gafarta masa.

Mafi girman abinda Annabi saw ya fada da sauran Annabawa bayan addua, shine

La’ilaha lllallahu wahdahu lasharika lahu lahul mulku, walahul hamdu wahuwa alah kulli sha’in, Qadirun

Kuma anfi so Alhaji kar yayi Azumi, don jin kafin tsayuwar arfa, ba za’ayi Magri da Isha’a filin arfa ba.

ZUWA MUZDALIFA:

1.Bayan faduwar rana ana filin Arfa, da sharadin a tabbata ta fadin

Daga nan, sai a tasarwa filin Musdalifa cikin cikar nazuwa, ba ture_ture

Amma yanzu dayake ana daukar Alhazai ne da motoci, to sai su Kira

Koda andade ba’a kawo mota ba, ko andade ba’a kwashe kuba ba komi

2. Ba za’ayi Sallolin Magriba da Isha’i, ba sai can koda lokaci yatafi

3. Abubuwan da zakayi a filin Muzdalifa:

Ya tabbata ya shiga cikin filin Arfa, kafin ya ajiye kayansa, akwai alamomi

*A fara yin Salloli kafin komi, dazarar an isa

Kuma za’ayi Magriba raka’a 3, Isha’i raka’a 2, Jam’i lokaci 1, kiran Sallah 1, Iqama 2

* Ya nemi abinci yaci idan yana bukatar haka

* Ya kwanta da wuri yayi bacci, don aikin dake gabansa gobe

Wajen baccin ba’arufe kai, kuma kar a shagaltu da fira, ko tsintar duwatsun jifa

4. Idan Asuba tayi sai ayi Sallar Asuba, cikin Jam’i, kuma sai a zauna gari ya waye

5. A nan ne, Allah yayi horo ayita zikirin Allah, a Mash’airl Haram, yanzu Masallaci ne

Za’a tsaya wajen ayita zikiri har sai rana tayi kusa 6ullowa, ana addua tareda daga hannuwa

Sai a bar filin kafin fitowar rana zuwa Mina don jifa.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment