KANUN LABARUN DUNIYAR YAU

▩ KANUN LABARUN DUNIYA 10-11-2018 ▩

◈ INEC ta wallafa sunayen ƴan takara na jihar Zamfara, babu ɗan takara ko ɗaya daga jam’iyyar APC.

◈ Sarkin Gummi, Justice Lawal Hassan ya koka kan salon yaki da rashawa irin na gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

◈ Gwamnatin Buhari ta gurfanar da tsohon Shugaban NDDC a gaban Kotu.

◈ Ana shirin fatattako wasu ɗaliban jihar Kano da ke karatu a waje.

◈ Uwar gidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta mika lambar yabo ga wata mai shara a filin jirgin sama na Abuja.

◈ Kwamitin Shugaban ƙasa ba shi da ikon kwace kadarori – Kotun daukaka ƙara.

◈ Magoya bayan Atiku sun gargaɗi Ezekwesili da kakkausar murya.

◈ Ƴan sanda sun damke wani da ke yaudarar mutane da sunan Atiku a Facebook.

◈ Ibrahim Shekarau ya ce ƴan Kwankwasiyya za su yi da-na-sani bayan 2019.

◈ Ƴan sanda a Lagos sun kama wani matashi da caka wa abokinsa kwalba a ciki kan ₦400.

◈ Kotu ta bayar da belin ɗan sandan da ya harbe ƴar uwar tsohuwar ministan kuɗi.

◈ Hukumar tattara kudaɗen haraji, FIRS ta tara Naira tirilyan 4.3 daga watan Janairu zuwa Oktoba.

◈ Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II zai gina katafaren kamfanin sarrafa iskar gas a jihar Akwa Ibom kan kuɗi $1.1 bilyan.

◈ Majalisar Tarayya ta amince da ƙudirin cire ka’idojin shekarun mai neman aiki.

◈ Hukumar Kwastam ta damke kwantena cike kayan Sojoji da makamai a jihar Rivers.

◈ Ƴan baranda sun kwace majalisar dokokin jihar Ondo bayan tsige kakaki.

◈ Majalisa za ta soke N-Power idan ya koma siyasa a cewar Shehu Sani.

◈ Bukola Saraki ya ce lallai Atiku Abubakar zai lashe zaben 2019 da gagarumin rinjaye.

◈ Ƴan Boko Haram sun kashe mutane tara har da soja a jihar Borno.

◈ Fayose ya ce muddin Buhari ya zarce za a shiga cikin matsanancin yunwa a Najeriya.

◈ Majalisa ta nemi a kori shugaban hukumar NEMA saboda salwantar da Naira bilyan 33.

◈ Majalisar wakilai za ta binciki badaƙalar da jam’iyyu suka yi a zaben fid da gwani.

◈ Hukumar zabe mai zaman kanta, INEC ta saki sunayen ƴan takarar gwamna 67 na zaben 2019.

◈ Dole Buhari ya saki Tiriliyan daya ga jami’o’in ƙasar nan kafin mu janye yajin aiki a cewar ASUU.

◈ Sowore ya ce Najeriya za tayi kuɗi da tabar wiwi idan ya zama Shugaban kasa.

◈ Mayakan Boko Haram sun kai ma matafiya harin kwantan bauna, sun kashe da dama a Borno.

◈ Ƴan Shi’a sun karyata Lai Mohammed kan cewa ana ciyar da shugabansu N3.5m duk wata.

◈ Shugaban ƙungiyar Boko Haram ya fitar da sabon bidiyo inda ya yi kaca-kaca da waɗanda su kace wai ya mutu. 

◈ Sanata Dino Melaye ya yi hasashen cewa tsohuwar jam’iyyarsa ta APC za ta tarwatse nan ba da jimawa ba.

◈ Majalisar dokoki na jihar Ogun ta tsige kakakinta, Bamidele David Oloyelogun da mataimakinsa.

◈ Ku mutunta doka – Hukumar Birtaniya ga ƴan Shi’a da hukumomin tsaro.

◈ Lauyoyi 120 ne za su tsayawa mutanen da ake zargi da kashe manjo janar Alkali.

◈ Ƴan bindiga sun kai wani hari a Birnin Gwari na jihar Kaduna.

◈ Gwamnatin tarayya ta ce yawaitar matasan da ba su da aikin yi na matuƙar barazana ga tsaro da cigaban Najeriya.

◈ Gwamna Ifeanyi Okowa ya bukaci ƴan Najeriya su mayar da al’amurransu ga Allah saboda shi kaɗai ne zai iya warware matsalolinsu.

◈ Musulmai a jihar Filato sun bukaci a ba su mukamin mataimakin gwamna.

◈ Ƴan bindiga sun sace ɗan takarar sanata da shugaban jam’iyyar ADC na jihar Ondo.

◈ Ma’aikatan hukumar filin jirgin sama sun yi barazanar shiga yajin aiki.

◈ An gargaɗi masu aikin zabe da ka da su ce za su hana a saci akwatin zabe, in an fara su bar wurin.

◈ Da takaici, yadda Najeriya ta zama ta 2 wajen yin kashi a bainar jama’a inji Buhari.

◈ Kasar Amurka ta yi ammana da irin shirye-shiryen da INEC ke yi domin zaben 2019

◈ Gwamnonin 6 ne suka bayyana cewar za su iya biyan N30,000 ma fi karanci albashi.

◈ Atiku Abubakar ya kara wa dukkan ma’aikatansa albashi na mafi karancin albashi na Naira 33,000.

◈ Buhari ya kaddamar da dokar-ta-baci a kan tsafta da samar da ruwa a Najeriya.

◈ Mutane 3 sun mutu, 5 sun yi bace a wani hatsarin jirgin ruwa.

◈ Sowore ɗan takarar shugaban kasa ya ce zai kama IBB da Obasanjo idan ya samu nasara.

◈ An kamo bakwai daga 13 da suka saci ma’aikaciyar lafiya a kwanakin baya a Yola.

◈ Kungiyar ƙwadago ta sake yin barazanar tafiya yajin aiki idan har gwamnatin tarayya ta yi kokarin canja baki kan N30,000.

◈ Hukumar DSS ta yi wa shugaban jam’iyyar APC na kasa tambayoyi kan zaben fid da gwani na jam’iyyar.

◈ Ɗan bindiga daɗi ya hallaka mutane a wani gidan shakatawa da ke Amurka.

◈ Ministan harkokin shari’ar ƙasar Amurka Jeff Session ya yi murabus daga mukaminsa.

◈ Jam’iyyar Republican ta shugaban Amurka ta rasa rinjaye a Majalisar Wakilan Kasar bayan zaben tsakiyar wa’adi. 

◈ An kashe dan majalisar Somaliya a wani harin bam a Mogadishu.

◈ Girgizar kasa mai karfin awo 5 da afku a kasar Ostireliya.

◈ Mahaukaciyar gobara na ci gaba da lakwame dazuzzuka da kuma rayukan al’umar Amurka.

◈ Shugaba Ali Bongo na Gabon ya farka daga doguwar suma da ya yi tun a watan Oktoba.

◈ Ebola na ci gaba da barna a Kongo.

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment