KANU LABARUN DUNIYA 

▦KANU LABARUN DUNIYA 6/11/2018▦

◈ Shugaba Buhari ya gana da wasu jiga-jigan gwamnati da kuma malaman addini.

◈ Gwamnan jihar Plateau, Simon Lalong ya bayyana cewar shugabanin al’umma da na addini ne suka ɗaurewa masu laifi gindi a jihar.

◈ Najeriya za ta cigaba da fitar da ganyen Zobo kasar Mexico.

◈ Majalisar dattawa ta kaddamar da bincike kan harin kisan da aka kai wa Ekweremadu.

◈ Yariman kasar Burtaniya, Charles da uwargidarsa sun iso Najeriya.

◈ Wasu sanatocin APC sun yi ganawar sirri da Shugaba Buhari a fadar gwamnatin tarayya.

◈ Kar ku raga wa masu furta kalaman batanci, ku cafke su – Buhari ga jami’an tsaro.

◈ Jam’iyyar APC mai mulki ta rasa wasu mambobinta guda huɗu a majalisar wakilai zuwa wasu jam’iyyun siyasa.

◈ Gwamnatin tarayya ta ce ba ta da isassun kuɗaɗen da za ta biya wa kungiyar ASUU bukatunsu.

◈ Majalisa ta ɗage takunkumin kin tantancen naɗe-naɗen shugaba Muhammadu Buhari.

◈ Daga gidan yari! Dariye ya jadadda goyon bayansa ga Buhari da Lalong a zabe mai zuwa.

◈ Yadda sojoji da ƴan sanda suka kashe ƴan Shi’a 492, rashin adalci ne a cewar Falana.

◈ Gwamnatin Najeriya ta karyata raɗe-raɗin canza Ministan kuɗi.

◈ Gamayyar ƙungiyoyin kwadago na kasa sun janye yajin aikin da suka tsara shiga a yau.

◈ Ministan kuɗi Zainab Ahmad ta rantsar da sababbin kwashinonin kotun daukaka kara na haraji.

◈ Ministan ilimi, Adamu Adamu ya roki Malaman jami’o’i da su janye yajin aikin da suke yi don a cigaba da tattaunawa.

◈ Gwamnan jihar Filato, Lalong ya roki Buratai ya yafewa al’ummar jiharsa na kisan Janar Idris Alkali.

◈ Gwamnati na ciyar da ƴan makaranta da kwai miliyan 6m da shanu 594 duk mako.

◈ Sojoji 149 ne ke fuskantar hukunci kan amfani da kafafen yada labarai na zamani ba bisa ka’ida ba.

◈ Hukumar INEC ta cire sunayen mutane 300,000 daga rijistar masu zabe.

◈ A jiya Litini manyan Malaman kasar Saudiyya suka ziyarci hedikwatan ƙungiyar Izala na kasa.

◈ Shugaban majalisar dattawa, Saraki ya karbi ƴaƴan jam’iyyar APC 5,000 da suka koma PDP a Kwara.

◈ Mutane biyu sun mutu sakamakon karyewar wata gada a garin Hanti-Mansiysk na kasar Rasha.

◈ Hukumar Bincike Kan Kayan Tarihi ta Indiya ta hana a yi Sallah a Masallacin Taj Mahal mai dimbin tarihi.

◈ Ɗalibai a Japan na kashe kansu saboda damuwa da ke damunsu.

◈ An rantsar da shugaba Paul Biya a wa’adi na bakwai a Kamaru. 

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment