KANUN LABARUN DUNIYA 5/11/2018

KANUN LABARUN DUNIYA 5/11/2018

◈ Majalisa ta gano wata badakalar kuɗi a NNPC da ka iya janyo a tsige shugaba Muhammadu Buhari.

◈ Kungiyar ASUU ta ce babu ruwanta da duk wani alkawari da gwamnati za ta sake dauka domin an sha su sun warke.

◈ Jam’iyyar APC ta yi kira ga a binciki ziyarar da Atiku ya kai Dubai.

◈ Rahoton da babban bankin Najeriya ya wallafa ya nuna cewar kuɗaɗen da kasar ke samu daga man fetur na raguwa.

◈ Kungiyar Shi’a ta saki jerin sunayen mambobinta 34 da Sojoji suka kashe.

◈ INEC ta haramtawa jami’anta shiga kungiyoyin WhatsApp(groups).

◈ Gwamnan jihar Filato ya je yi wa Buratai ta’aziyyar kisan Manjo Janar Idris Alkali a yau.

◈ Peter Obi ya kai wa Sanata Rabiu Kwankwaso ziyara a Abuja

◈ Atiku ya kalubalanci Buhari kan kyautar Dala 500,000 da ya bai wa Guinea Bissau.

◈ Gwamnonin APC za su hadu da sanatocin jam’iyyar don tsige Oshimhole.

◈ Za a buɗe katafren kamfanin sarrafa tumatur a jihar Katsina.

◈ Yan JTF sun yi nasarar kashe ƴan Boko Haram da dama a karamar hukumar Gubio jihar Borno.

◈ Ƙungiyar malaman jami’o’i, ASUU ta shiga yajin aiki sai Baba-ta-gani a yau.

◈ Ƙungiyar SERAP ta bukaci Buhari ya sanya baki a harkallan bidiyon Ganduje.

◈ Rundunar ƴansanda a jihar Filato ta nuna mutane 19 da ake zargi da kisan Manjo Janar Idris Alkali.

◈ An kasa samun matsaya tsakanin gwamnati da kungiyoyin ƙwadago.

◈ Yarima Charles na Ingila zai kawo ziyara Najeriya a makon nan inda zai gana da Buhari kan tsaro. 

Published by jekadiyarzamfara

Wannan shafi an bude shine domin sanar da ku halin da duniya take ciki tare da ilmantarwa da nishadantarwa. Ga masu sha'awar turo muna sakonninsu suna iya turo muna sakon Email; - Jekadiyarzamfara@gmail.com A tabbata ana da sahihancin labarin da za'a turo muna tare da shaidar hotuna ko video. Mun gode da kasancewa da jekadiyarzamfara

Leave a comment